fidelitybank

Najeriya ta bukaci Iran da Isra’ila su tsagaita rikici a tsakanin juna

Date:

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta yi kira da dukkan bangarorin da ke da hannu a sabon rikici a yankin Gabas ta Tsakiya da su tsagaita wuta.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da kakakin ma’aikatar harkokin wajen Najeriya Francisca Omayuli ta fitar a ranar Lahadi a Abuja.

“Gwamnatin tarayyar Najeriya ta bi sahun sauran kasashen duniya da su yi kira ga Iran da Isra’ila da su yi taka-tsan-tsan, yayin da ake ci gaba da kokarin diflomasiyya na sassauta rikici da kaucewa barkewar rikici a Gabas ta Tsakiya.

Sanarwar ta ce, “A cikin wannan mawuyacin lokaci, ya kamata kasashen biyu su yi tunani a kan kudurin da kasashen duniya suka dauka na warware rikice-rikice cikin lumana, domin ci gaban zaman lafiya da tsaro a duniya.”

A halin da ake ciki kuma, shugabannin kasashen duniya ma sun bukaci a dage bayan Iran ta harba makami mai linzami da ba a taba ganin irinta ba, tare da kai hari da jirage marasa matuka kan babbar abokiyar gabarta ta Isra’ila cikin dare, a daidai lokacin da yakin Gaza ya kara ruruta wutar rikicin Gabas ta Tsakiya.

Shugabannin kasashen G7 a ranar Lahadi sun yi Allah wadai da harin da Iran ta kai wa Isra’ila ba tare da bata lokaci ba, tare da yin alkawarin ci gaba da kokarin kawo karshen ta’addanci. “Kawo karshen rikicin a Gaza da wuri-wuri, musamman ta hanyar tsagaita wuta nan take, zai kawo sauyi.”

Shugabannin sun ba da cikakken goyon bayansu ga Isra’ila, suna masu cewa a shirye suke su “daukar karin matakai” a matsayin mayar da martani ga “karin sabbin tsare-tsare.”

Iran ta kaddamar da harin, wanda shi ne na farko da aka taba kaiwa kai tsaye kan yankin Isra’ila, a matsayin ramuwar gayya ga wani mummunan harin da aka kai ta sama da Isra’ila ke zargi da lalata ginin ofishin jakadancinta a babban birnin Syria a farkon wannan wata.

A halin da ake ciki kuma, Isra’ila da kawayenta sun kame akasarin makaman da ke shigowa, in ji rundunar sojin Isra’ila, inda ta bayar da rahoton cewa mutane 12 da suka jikkata kuma ba a samu asarar rai ba, amma harin ya kara tsananta fargabar harin da Isra’ila ta kai.

cnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Hogan ya mutu bisa cutar gazawar koda

An bayyana cikakkun bayanai game da mutuwar ɗan wasan...

Sojoji sun kashe rikaken dan Bindiga Dan Dari Biyar a Sokoto

Dakarun Operation FANSAR YANMA sun yi nasarar fatattakar wani...

An kashe utane 30 a yakin Thailand da Cambodia

An shiga kwana na uku na faɗan kan iyaka...

Ba mu ƙayyade shekarun shiga ƙaramar sakandare JSS1 – Ma’aikatar Ilimi

Ma'aikatar Ilimi a Najeriya ta musanta rahoton da wasu...

Ido da Ido na ga yadda Sojojin Isra’ila ke kashe Falasdinawa – Tsohon Sojin Amurka

Wani tsohon sojan Amurk ya ce, ya ga yadda...

‘Yan majalisar Birtaniya 220 na neman ƙasar ta amice da ƙasar Falasɗinu

'Yan majalisar Birtaniya 220 sun nemi gwamnatin ƙasar ta...

Buhari yaki karbar kyautar Agogon lu’u-lu’u da jirgin sama – Garba Shehu

Mai magana da yawun tsohon Shugaban Najeriya Muhammad Buhari,...

An kama wanda ya kashe tsohuwar Matarsa a Jigawa

Ƴansandan Jihar Jigawa sun ce, sun kama wani mutum...

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan Kwankwaso

Fadar shugaban kasa, ta mayar wa tsohon gwamnan Kano...

Barau FC ta naɗa Ladan Bosso sabon kocinta

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barau FC ta sanar da...

Am fara dawo da ‘yan Najeriya daga Afrika ta Tsakiya

Hukumomi a Najeriya sun ce, sun fara ƙoƙarin mayar...

G-Fresh da Hamisu Breaker sun samu gurbi kurkuku bayan sun watsa Naira

Babbar kotun tarayya da ke jihar Kano ɗaure shahararrun...
X whatsapp