fidelitybank

Najeriya ta ƙara yawan man fetur da take haƙowa zuwa ganga 70,000

Date:

Najeriya ta ƙara yawan man fetur da take haƙowa zuwa ganga 70,000 a kowace rana fiye da adadin da ƙungiyar OPEC ta sanya mata, kamar yadda nazarin kamfanin dillancin labarai na Reuters ya nuna.

A cewar nazarin, man da ƙasashe mambobin ƙungiyar OPEC – ta masu arzikin man fetur – su ka fitar a watan Fabrairu ya ƙaru, inda Iran ke kan gaba, duk da ƙoƙarin da Amurka ke yi na daƙile fitar da man.

Najeriya ta ƙara adadin man da take fitarwa da ya zarce adadin da ƙungiyar ta ware mata.

Ƙungiyar ta OPEC ta haƙo gangan miliyan 26 da 74,000 a kowace rana a watan da ya gabata, inda aka samu ƙarin ganga 170,000 a kullum idan aka kwantanta da watan Janairu, a cewar nazarin na Reuters.

Ƙungiyar OPEC+ – wadda ta haɗa da ƙasashen OPEC da Rasha da sauran ƙawaye – na son rage yawan man da suke haƙowa a watan Maris sakamakon hasashen raguwar buƙatar man da kuma wayan fitar da man daga ƙasashen da ba sa cikin ƙungiyar.

To sai dai a ranar Litinin, ta yanke shawarar dakatar da shirin nata, inda take sa ran ƙara yawan man da take haƙowa a watan Afrilu.

Nazarin ya gano cewa ƙasar Iran ce kan gaba a wajen haƙo man, inda take haƙo ganga 80,000 a kowace rana, a cewar nazarin Reuters.

Fitar da ɗanyan mai daga Iran ya farfaɗo lokacin gwamnatin tsohon shugaban Amurka, Joe Biden duk da takuntuman Amurka, sai da ƙarkashin shugaba Donald Trump, Amurka na sabunta ƙoƙarinta na katse fitar da man baki-ɗaya.

vanguard (nigeria)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Muƙarraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon ɗan majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...

An binne marigayi Muhammadu Buhari a gidansa na Daura

An binne gawar tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari a...

Pillars ta dauki yan wasa guda biyu

Kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars ta tabbatar da...

An cafke ‘yan Daba 28 a Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce ta samu...

Na yafe wa Buhari duk abun da ya yi min – Buba Galadima

Buba Galadima, wanda tsohon abokin marigayi Muhammadu Buhari ne...

Shugabannin Afrika za su halarci jana’izar Buhari

Ana sa ran wasu daga cikin shugabannin ƙasashen Afirka...

Yadda ake shirye-shiryen jana’izar Buhari a Daura

A yanzu haka dai alumma na ta tururuwa domin...
X whatsapp