Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin aikin shimfiɗa bututun gas zuwa nahiyar Turai.
Mataimakin Sugaban ƙasa, Kashim Shettima ne ya bayyana hakan yayin ganawarsa da shugaban kamfanin Vitol Group a fadar shugaban ƙasa ranar Litinin.
Aikin bututun wanda zai bi ta ƙasar Morocco, za a yi amfani da shi wajen sayar wa ƙasashen Turai iskar gas, yayin da suke yunƙurin rage dogaro da Rasha a fannin makamashi.
Mataimakin shugaban ya nemi masu zuba jari na ƙasashen duniya da su zuba kuɗaɗensu a Najeriya, yana mai cewa Shugaban Ƙasa Bola Tinubu “na aikin saita Najeriya”.