fidelitybank

Najeriya na buƙatar Tiriliyan 21 don gina gidaje – Shettima

Date:

Najeriya na buƙatar naira tirliyan 21 don cike giɓin da take da shi a ɓangaren gidaje, duk da ƙoƙarin matakan gwamnati uku.

Mataimakin shugaban Najeriya Sanata Kashim Shettima ne ya bayyana haka a Sokoto, lokacin ƙaddamar da bikin gina rukunin gidaje guda 500 da gwamnatin jihar ta ɓullo da shi.

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN ya ambato Kashim Shettima na yaba wa Gwamna Ahmed Aliyu na Sokoto, saboda ƙoƙarinsa wajen magance buƙatun gidaje a tsakanin al’ummar jihar, ya ma nunar da cewa giɓin gidajen da ake da shi a Najeriya, wani babban ƙalubale ne.

”Najeriya na da giɓin gida miliyan 28 kuma za mu buƙaci naira tirliyan 21 don cimma buƙatun gidajen da muke da su. Wannan mataki da gwamna ya faro, babban abin yabawa ne kuma ya cancanci koyi daga sauran gwamnatocin jihohi.

Tun da farko, gwamnan ya bayyana cewa gwamnatin jihar Sokoto na gina rukunin gidajen ne saboda ma’aikata, kuma za a sayar musu da su ne da zarar an kammala aikin a kan tsarin ɗan haya ya mallaka.

legit.ng.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp