Tsohon shugaban majalisar dattawa kuma dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC), Cif Ken Nnamani, ya bayyana cewa, shugaban kasa mai jiran gado bayan shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sauka dole ne ya zama shugaba amintacce.
Nnamani ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi ga gamayyar kungiyoyin matasa da magoya bayan shiyyoyin siyasa shida na Najeriya da suka ziyarci ofishin yakin neman zaben sa na Abuja, domin nuna goyon bayansu ga burinsa na zama shugaban kasa.
Tsohon dan majalisar ya ce, ya yanke shawarar neman jam’iyyar APC, a zaben fidda gwani na shugaban kasa a ranar 29 ga watan Mayu, 2022, don samar da ingantaccen shugabanci, idan aka zabe shi shugaban kasa, wanda zai hada kan kasar nan, da zurfafa dimokaradiyyar ta da sake gina hanyoyin zamantakewa da tattalin arziki, don samun ci gaba mai dorewa, akan samarwa da kuma rarraba damammaki da albarkatu cikin adalci, a fadin shiyyoyin siyasar Najeriya.
Ya ce, Najeriya a halin da take ciki a halin yanzu, tana bukatar shugaba da aka gwada kuma amintace.