Ministan lafiya Farfesa Muhammad Pate, ya ce arziƙin da ƙasar nan take asara a shekara sakamakon cutar zazzaɓin cizon sauro (maleriya) ya zarta dala biliyan 1.1.
Pate ya bayyanna hakan ne kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito, yayin ƙaddamar da taron bayar da shawarwari da tuntuɓa kan yaƙi da cutar ta maleriya a Najeria, wanda aka yi a Abuja.
A wata sanarwa da mataimakin darektan yaɗa labarai na ma’aikatar, Alaba Balogun, ya fitar a yau Talata, ya ce Farfesa Pate ya ce maleriya ba matsala ce ta rashin lafiya ba kaɗai ta zama matsala ga tattalin arziƙi da cigaba wadda ya kamata a ɗauki ƙwararan matakan yaƙi da ita.
Ya ce, maleriya na ci gaba da gagarumar illa a kan Najeriya, inda take da kashi 27 cikin ɗari na yawan mutanen da ke kamuwa da cutar a duniya, da kuma kashi 31 cikin ɗarin na yawan mutanen da ke mutuwa a duniya a dalilinta .
Ministan ya ƙara da cewa Najeriya ce ta fi fama da matsalar wannan cuta, inda a 2022, sama da yara ‘yan ƙasar 180,000 ‘yan ƙasa da shekara biyar suka mutu a sanadiyyar cutar – ”wanda wannan abu ne da za mu iya kauce wa.” In ji ministan.