fidelitybank

Najeriya da Jamus sun ƙulla yarjejeniyar samar da wutar lantarki

Date:

Najeriya da Jamus sun amince da kara yawan ƙarfin wutar lantarki watts miliyan 12, ta hanyar shirin samar da wutar lantarki na shugaban kasa (PPI).

Shirin samar da wutar lantarki wanda gwamnatin tarayya za ta samar da rancen bashi zuwa kasashen waje a halin yanzu da wasu bankunan kasar Jamus ke yi wa Najeriya, zai lakume kusan dala miliyan 60 kuma zai hada da siyan tiransifoma 10 da tashoshi guda 10.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu da shugaban gwamnatin Jamus, Olaf Scholz, duk sun jagoranci rattaba hannu kan yarjejeniyar a ranar Juma’a a birnin Dubai na Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE), a gefen taron Majalisar Dinkin Duniya Climate Conference (COP28) a Expo City.

Manajan Daraktan Kamfanin Lantarki na Gwamnatin Tarayya, Kenny Anue ne ya sanya hannu a madadin Najeriya yayin da Nadja Haakansson, Manajan Darakta (Africa) Siemens AG, ya sanya hannu a madadin Siemens.

Anue ya jaddada kudirin shugaban kasa, Tinubu na inganta samar da wutar lantarki a Najeriya, inda ya jaddada cewa ya nanata cewa samar da ababen more rayuwa na da matukar muhimmanci ga sauye-sauyen da ake yi.

Ya bayyana cewa makamashi da kudade suna tsakiyar manufar sake fasalin tattalin arziki na gwamnati kuma PPI, ta hanyar tsarawa, ta ƙunshi sassan biyu tare da goyon bayan abokan hulɗa, Siemens Energy da masu kudi da gwamnatin Jamus ke goyon bayan.

Da yake jawabi ga shugaban kasa, Anue ya ce: “Ya shugaban kasa, tare da kwazonka da jajircewarka ta hannun Maigirma Ministan Wutar Lantarki, yanzu muna neman yin amfani da ko kuma aiwatar da abin da ya rigaya ya kasance wani shiri mai amfani a shirin ikon shugaban kasa ta hanyar wannan yarjejeniya mai karfi a yau.”

www.legit news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp