fidelitybank

Najeriya da Indiya za su haɗa kai na yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi

Date:

Hukumar hana sha da fatauncin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya, NDLEA da takwararta ta India, sun amince da ƙara haɗa kai wajen yaƙi da safarar muyigun ƙwayoyi tsakanin ƙasashen biyu.

Hakan na cikin batutuwan da shugabannin hukumomin, Birgediya janar Buba Marwa mai ritaya da Mista Anurag Garg su ka amince da su a lokacin wata tattaunawa da suka yi ta intanet.

Sun ce za su fi mayar da hankali ne kan yadda ake shigar da haramtattun magunguna kamar tramadol da magunguna masu hodar ibilis cikin Najeriya daga Indiya.

Buba Marwa ya ce irin waɗannan ƙwayoyi na da illa matuƙa kan lafiya da tsaro a ƙasashen biyu, ya kuma ce akwai buƙatar hukumomin biyu su ƙara ƙarfafa alaƙarsu bisa la’akari da yarjejeniyar fahimta da suka sanya wa hannu a 2023.

Ya kuma buƙaci hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta Indiya NCB ya taimaka wajen bai wa jami’ansa horo na musamman.

Najeriya na daga ƙasashen duniya da suka yi ƙaurin-suna wajen sha da safarar miyagun ƙwayoyi, abin da ya sa gwamnatin ƙasar ɗaukar matakai daban-daban ciki har da kafa ita hukumar ta NDLEA.

tribune news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaɗi masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga Falasɗinawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...

Lauyan Sowore ya bukaci a sake shi cikin gaggawa

Lauyoyin ffitaccen ɗan gwagwarmayar nan kuma ɗan jarida, Omoyele...

Najeriya da Indiya za su haɗa kai na yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fatauncin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu,...
X whatsapp