fidelitybank

Najeriya ce ƙasa ta biyu a duniya da ƴan ƙasar suka shiga Birtaniya aikin yi

Date:

Wani rahoto da ofishin kula da ƙididdiga na Birtaniya ya fitar, ya ce Najeriya ce ƙasa ta biyu mafi yawan mutanen da suka yi tururuwa zuwa Birtaniyan a shekara ta 2024.

Alƙaluman rahoton sun nuna cewa ƴan Najeriya 120,000 ne suka kwarara zuwa Birtaniya a 2024.

Lamarin na nuna cewa ƙasar tana biye da Indiya da ke matsayi na farko a jerin, inda mutanen ta 240,000 suka shiga Birtaniyar.

Rahoton ya ce batun neman aikin yi yana cikin abubuwan da ke sa ƴan Najeriya tururuwar zuwa Birtaniya.

Dakta Ishaku Shitu Al-Mustapha,wani babban malami a jami’ar Canterbury Christ da ke birnin Landan, ya ce neman kyautatuwar rayuwa, kuma su na cikin abin da ya sa ƴan Najeriya ke ƙaura zuwa Birtaniyar.

“Wasu ƴan Najeriya sun gaji da ƙasar, ga rashin shugabanci na gari da kuma rashin albashi mai kyau su ma suna cikin abin da ya ƴan ƙasar ke ficewa daga cikinta,” in ji Dakta Al-Mustapha.

Ya ce samun shugabanni masu kishin ƙasa da kuma tsoron Allah zai sa ƴan Najeriya su rage fita zuwa ƙasashen waje.

nan news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Yunwa na kara tsananta a arewa maso gabashin Najeriya – ICRC

Kungiyar agaji ta Red cross (ICRC) ta bayyana yadda...

Ba zan taba watsawa Tinubu kasa a ido ba – IBB

Ɗan tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, wato...

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar...

Za a yi ruwan sama da iska mai ƙarfi a jihohi harda Kano – NiMET

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ta fitar...

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...

Mu na gargadin Isra’ila kan korar al’ummar Gaza daga yankin su – MDD

Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya...

Rikici ya kuma balle a Syria

Ƙungiyoyin kare haƙƙin dan'adam sun ce, wani sabon rikici...

Tsofaffin ‘Yansanda na da ‘yancin yin zanga-zanga – A Cewar Amnesty

Ƙungiyar Amnesty International ta ce tsofaffin ƴansandan Najeriya girmamawa...

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haɗaka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...
X whatsapp