Babban kocin Afirka ta Kudu, Hugo Broos, ya bayyana kwarin gwiwar cewa Najeriya za ta taimaka wa tawagarsa wajen samun tikitin shiga gasar cin kofin duniya ta 2026.
Kungiyar Broos ta bude tazarar maki biyu a rukunin C na wasannin neman tikitin shiga gasar cin kofin duniya na 2026.
Hakan ya biyo bayan nasarar da suka samu da Lesotho da ci 2-0 a filin wasa na Peter Mokaba da yammacin Juma’a.
A daya bangaren kuma Najeriya ta lallasa Rwanda da ci 2-0 a Kigali, inda Victor Osimhen ya zura ta biyu.
Super Eagles dai tana bayan Afrika ta Kudu da ke kan gaba a rukunin C da maki hudu.
Da yake magana da manema labarai bayan da tawagarsa ta doke Lesotho, Broos ya yi nuni da cewa kungiyar Eric Chelle ba za ta iya daina samun maki a wasannin share fagen shiga gasar ba, kuma za ta jajirce sosai a kowane wasa, tare da taimakawa Afirka ta Kudu a cikin wannan tsari.
“Kun san na fada kwanakin baya cewa akwai wata kungiya ko kasa a cikin kungiyar da za ta iya taimaka mana sosai kuma Najeriya ce, kun ga sun doke Rwanda a yau,” in ji Hugo Broos a taron manema labarai bayan wasan.
“Ba za su iya sake samun damar rasa maki ba, a kowace kungiya za su yi duk abin da za su yi don samun nasara kuma a halin yanzu muna da maki hudu a gaban Najeriya.
“Ya rage namu mu yi abin da ya kamata mu yi, kuma idan muka yi haka, Najeriya za ta taimake mu – za ku gani.”