An bayyana Najeriya a matsayin kasar da ke kan gaba wajen samar da mai a nahiyar Afirka, kuma daya daga cikin manyan kasashe uku masu samar da iskar gas, in ji wani rahoto na African Energy Chambers (AEC).
Rahoton ya tabbatar da cewa da alama Najeriya za ta ci gaba da rike wannan matsayi a rubu’in farko na wannan shekara, yayin da matsayinta na daya daga cikin manyan kasashe uku masu samar da iskar gas zai ci gaba da kasancewa har zuwa shekarar 2025.
Najeriya ta na daya daga cikin manyan masu nauyi a Afirka idan aka zo batun hakowa da samar da iskar gas mai sama da ganga biliyan 36 da triliyan 200 na iskar gas, kasar ta yi nasarar sanya kanta a matsayin babbar kasuwa mai kayatarwa da kuma samar da gas
Bisa hasashen da aka yi, Najeriya za ta hako gangar danyen mai miliyan 1.46 a kowace rana daga cikin ganga miliyan 6.35 da nahiyar Afirka baki daya za ta hako a kowace rana, lamarin da zai sake tabbatar da matsayin kasar a matsayin cibiyar makamashin nahiyar a matsayin samar da shi a yammacin Afirka mafi kololuwa a 2023.