Wani rahoto da ofishin kula da ƙididdiga na Birtaniya ya fitar, ya ce Najeriya ce ƙasa ta biyu mafi yawan mutanen da suka yi tururuwa zuwa Birtaniyan a shekara ta 2024.
Alƙaluman rahoton sun nuna cewa ƴan Najeriya 120,000 ne suka kwarara zuwa Birtaniya a 2024.
Lamarin na nuna cewa ƙasar tana biye da Indiya da ke matsayi na farko a jerin, inda mutanen ta 240,000 suka shiga Birtaniyar.
Rahoton ya ce batun neman aikin yi yana cikin abubuwan da ke sa ƴan Najeriya tururuwar zuwa Birtaniya.
Dakta Ishaku Shitu Al-Mustapha,wani babban malami a jami’ar Canterbury Christ da ke birnin Landan, ya ce neman kyautatuwar rayuwa, kuma su na cikin abin da ya sa ƴan Najeriya ke ƙaura zuwa Birtaniyar.
“Wasu ƴan Najeriya sun gaji da ƙasar, ga rashin shugabanci na gari da kuma rashin albashi mai kyau su ma suna cikin abin da ya ƴan ƙasar ke ficewa daga cikinta,” in ji Dakta Al-Mustapha.
Ya ce samun shugabanni masu kishin ƙasa da kuma tsoron Allah zai sa ƴan Najeriya su rage fita zuwa ƙasashen waje.