fidelitybank

Najeriya ba ta sanya hannu ba a kan yarjejeniyar auren jinsi ba – Gwamnati

Date:

Gwamnatin Najeriya ta tabbatar da sanya hannu kan Yarjejeniyar Samoa, tana mai cewa ta ƙunshi ayyukan cigaban al’umma ne ba amincewa da auren jinsi ko kuma kare haƙƙin ‘yan luwaɗi ba.

A ranar Laraba ne wasu rahotonni suka ambato cewa gwamnatin tarayya ta saka hannu kan yarjejeniyar, wadda ta ƙunshi wasu alƙawurra tsakanin ƙasashen Tarayyar Turai, da gamayyar ƙasashen yankin Karebiya da na Pacific .

Rahotonnin sun ambato cewa baya ga ayyukan raya ƙasa da cigaban al’umma, yarjejeniyar ta kuma ƙunshi batun amincewa da gwagwarmyara neman ‘yanci da masu fafutikar luwaɗi da maɗigo ke yi a ƙasashen.

Sai dai cikin wata sanarwa, ma’aikatar yaɗa labarai ta ce Najeriya ta bayyana ƙarara cewa “ba za ta yarda da duk tanadin da ya saɓa wa dokar Najeriya ba” kafin ta saka hannu.

“Ya zama wajibi mu tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa gwamnatin Bola Tinubu… ba za ta saka hannu kan wata yarjejeniya ba da za ta ci karo da muradan mutanenta ba,” a cewar Ministan Yaɗa Labarai Mohammed Idris cikin wata sanarwa a yammacin yau Alhamis.

“Kafin amincewa da yarjejeniyar, wakilanmu sai da suka tsefe duka alƙawuran da aka yi tsakanin Tarayyar Turai da ƙasashen OACPS.

“Yarjejeniyar ba wani abu ba ce illa tsarin shari’a da zai ba da damar haɗin gwiwa tsakanin OACPS da Tarayyar Turai domin cigaban al’umma, da daƙile sauyin yanayi, da samar da kuɗaɗen zuba jari.”

A shekarar 2014 Najeriya ta amince da dokar haramta alaƙar aure tsakanin jinsi ɗaya, abin da ke nufin luwaɗi da maɗigo haramtattu ne a ƙasar.

legitnews.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp