Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya bada tabbacin cewa Naira za ta ci gaba da yin tsada idan aka kwatanta da dala.
Shettima ya ce shugaba Bola Tinubu ya fahimci wasan kuma zai tabbatar da cewa Naira ta ci gaba da daraja.
Mataimakin shugaban kasar ya bayyana haka ne a lokacin da tawagar kungiyar ‘yan kasuwa da masana’antu ta Legas, karkashin jagorancin shugabanta, Gabriel Idahosa ta kai masa ziyarar ban girma a ofishinsa da ke fadar shugaban kasa ta Villa, Abuja.
Wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Stanley Nkwocha ya fitar, ta ruwaito mataimakin shugaban kasar na cewa dole ne Tinubu ya kawo karshen tallafin man fetur da kuma tabbatar da hadewar kudaden musaya da dama domin a baya tsarin yana samar da hamshakan attajirai cikin dare.
Ya ce: “Naira ta tafi haywire wasu mutane suna biki amma a ciki muna yi musu dariya saboda mun san cewa muna da shugabanni da za su sauya salon tafiyar.
“Asiwaju ya san wasan, kuma da gaske Naira na karuwa kuma bambancin zai kara raguwa.”
Mataimakin shugaban kasar ya kuma bayyana cewa, irin jagoranci da Tinubu ya samar a matsayin gwamnan Legas ya sa harsashin ci gaban da aka samu a jihar.
“A koyaushe za mu gode wa Shugaba Tinubu saboda samar da tsarin ci gaban Legas da muke gani a yau,” in ji shi.