fidelitybank

Naira za ta ci gaba da yin nasara a kan dalar Amurka – Shettima

Date:

Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya bada tabbacin cewa Naira za ta ci gaba da yin tsada idan aka kwatanta da dala.

Shettima ya ce shugaba Bola Tinubu ya fahimci wasan kuma zai tabbatar da cewa Naira ta ci gaba da daraja.

Mataimakin shugaban kasar ya bayyana haka ne a lokacin da tawagar kungiyar ‘yan kasuwa da masana’antu ta Legas, karkashin jagorancin shugabanta, Gabriel Idahosa ta kai masa ziyarar ban girma a ofishinsa da ke fadar shugaban kasa ta Villa, Abuja.

Wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Stanley Nkwocha ya fitar, ta ruwaito mataimakin shugaban kasar na cewa dole ne Tinubu ya kawo karshen tallafin man fetur da kuma tabbatar da hadewar kudaden musaya da dama domin a baya tsarin yana samar da hamshakan attajirai cikin dare.

Ya ce: “Naira ta tafi haywire wasu mutane suna biki amma a ciki muna yi musu dariya saboda mun san cewa muna da shugabanni da za su sauya salon tafiyar.

“Asiwaju ya san wasan, kuma da gaske Naira na karuwa kuma bambancin zai kara raguwa.”

Mataimakin shugaban kasar ya kuma bayyana cewa, irin jagoranci da Tinubu ya samar a matsayin gwamnan Legas ya sa harsashin ci gaban da aka samu a jihar.

“A koyaushe za mu gode wa Shugaba Tinubu saboda samar da tsarin ci gaban Legas da muke gani a yau,” in ji shi.

legit news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp