fidelitybank

Naira miliyan 44.2 sun yi batan dabo wajen sayen fom din takarar APC

Date:

Jam’iyar APC na binciken yadda Naira miliyan 44.2 suka yi batan dabo ranar Laraba a sakatariyar jam’iyar da ke Abuja.

Batan kudin ya janyo dakatar da sayar da fom din ‘yan takara, musamman ‘yan takarar da ke son tsayawa takarar mukaman ‘yan majalisar wakilai da na dattawa.

Jam’iyyar ta kafa wasu rumfuna, domin sayar da fom din ga masu son tsayawa takara.

Sai dai da misalin karfe 4:15, jam’iyyar ta cire rumfunan kuma ta umarci ma’aikatanta su ci gaba da sayar da fom din a cibiyar gudanar da taruka ta International Conference Centre da ke Abuja.

Jaridar Daily Post ta ce wannan matakin ya biyo bayan bacewar dalar Amurka 75,000 ne wanda yayi daidai da Naira miliyan 44.2.

Wani ma’aikacin jamiyyar da baya son a bayyana sunansa ya ce, an cire rumfunan ne bayan da aka gane kudaden sun yi batan dabo.

Ma’aikacin ya ce “Mun ji cewa wani mutum da yazo sakatariyar jam’iyyar, sai dai saboda yawan jama’a bai iya shiga cikin ginin ba da motarsa. Amma yayin da yake kokarin shiga cikin ginin, mun ji wai wani ambulan da yake dauke da shi wanda dala 75,000 ke ciki ya fadi.”

nhgsfp

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...
X whatsapp