fidelitybank

Nahiyar Turai su ma za mu kakaba musu haraji – Trump

Date:

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce ko shakka babu zai ƙara haraji kan kayan da ake ƙerawa ake shiga da su Amurka daga Tarayyar Turai.

Mista Trump ya shaida wa manema labarai cewa zai sanya harajin nan ba da jimawa ba, ya kuma zargi kungiyar da cin gajiyar Amurka, yana mai bayyana hakan a matsayin zalunci.

”Ba su sayen motocinmu da amfanin gonarmu, kusan babu wani abu da suke saya daga wajenmu, amma mu kusan komai daga wajensu muke saye” in ji shi.

A yau Litinin ne ya kamata shugaba Trump ya tattauna da shugabannin ƙasashen Canada da Mexico bayan sanya wa ƙasashen biyu masu maƙwaftaka da Amurka haraji da kuma China.

Tun da farko dai Trump ya gargaɗi Amurkawa cewa matakin nasa zai iya haifar da raɗaɗi, sai dai ya ce nan gaba hakan zai zama alheri ga Amurka.

tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp