fidelitybank

NAFDAC ta buƙaci a riƙa yanke wa masu jabun magunguna hukuncin kisa

Date:

Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna, NAFDAC ta nemi hukuncin kisa ga masu haɗawa da shigar da jabun magunguna.

A cewar shugabar hukumar Mojisola Adeyeye, tsauraran matakai ne kawai za su hana aikata hakan musamman idan lamarin na kai wa ga mutuwar yara.

”Wani ya sayi magani naira 13,000 a wani kanti, wani kuma ya sayi irin wannan maganin a wani shagon kan naira 3,000, hakan ya ankarar da mu, kun san mene ne? da muka gwada maganin a ɗakin gwaje-gwajenmu da ke Kaduna, babu wani sinadarin magani mai amfani a cikin shi, a don haka ina son a fara aiwatar da hukuncin kisa,” in ji ta a wani hira da gidan talibijin na Channels.

Ko a jiya ma majalisar wakilai ta buƙaci babban mai shari’a na tarayya da ya gabatar da tsauraran takunkumai da suka hada da ɗaurin rai da rai ga masu haɗawa da masu shigo da magungunan jabu cikin ƙasar.

Bayan muhawara kan ƙudurin wanda ya samu goyon bayan ƴan majalisar, majalisar ta buƙaci babban lauyan gwamnatin tarayya da ya gabatar da gyara ga dokokin da ake da su da nufin zartar da hukunci mai tsauri.

nigeria daily post

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp