fidelitybank

NAFDAC ta buƙaci a riƙa yanke wa masu jabun magunguna hukuncin kisa

Date:

Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna, NAFDAC ta nemi hukuncin kisa ga masu haɗawa da shigar da jabun magunguna.

A cewar shugabar hukumar Mojisola Adeyeye, tsauraran matakai ne kawai za su hana aikata hakan musamman idan lamarin na kai wa ga mutuwar yara.

”Wani ya sayi magani naira 13,000 a wani kanti, wani kuma ya sayi irin wannan maganin a wani shagon kan naira 3,000, hakan ya ankarar da mu, kun san mene ne? da muka gwada maganin a ɗakin gwaje-gwajenmu da ke Kaduna, babu wani sinadarin magani mai amfani a cikin shi, a don haka ina son a fara aiwatar da hukuncin kisa,” in ji ta a wani hira da gidan talibijin na Channels.

Ko a jiya ma majalisar wakilai ta buƙaci babban mai shari’a na tarayya da ya gabatar da tsauraran takunkumai da suka hada da ɗaurin rai da rai ga masu haɗawa da masu shigo da magungunan jabu cikin ƙasar.

Bayan muhawara kan ƙudurin wanda ya samu goyon bayan ƴan majalisar, majalisar ta buƙaci babban lauyan gwamnatin tarayya da ya gabatar da gyara ga dokokin da ake da su da nufin zartar da hukunci mai tsauri.

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp