Shugaban kasa Muhammadu Buhari a ranar Asabar, ya nuna alhinin rasuwar tsohon shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Vincent Ogbulafor.
Buhari, a cikin sakon ta’aziyya ga iyalan Ogbulafor, ya yi imanin cewa za a tuna da Ogbulafor saboda rawar da ya taka a ci gaban dimokuradiyyar Najeriya.
Tsohon shugaban jam’iyyar PDP na kasa ya rasu a kasar Canada ranar Juma’a yana da shekaru 73 a duniya.
Sai dai shugaban ya jajantawa shuwagabanni da ‘ya’yan jam’iyyar PDP, da gidan sarautar Olokoro da ke Umuahia, da gwamnati da al’ummar jihar Abia bisa rashin tsohon sakataren jam’iyyar na kasa.
A wata sanarwa dauke da sa hannun mai magana da yawunsa, Garba Shehu, Buhari ya yi imanin cewa za a tuna da tsohon shugaban PDP na kasa bisa rawar da ya taka wajen ci gaban dimokuradiyyar kasa.
Shugaban ya yabawa kishin Yariman Olokoro wajen wanzar da hadin kai da ci gaban kasa.
Shugaba Buhari ya yi addu’ar Allah ya karbi ran wadanda suka rasu ya kuma baiwa iyalansa lafiya.