fidelitybank

Na yi gwarwagdon yi na ga ‘yan Najeriya – Buhari

Date:

Shugaban kasa Muhammadu Buhari a ranar Litinin din nan, ya ce, ya yi alkawarin yi wa ‘yan Najeriya hidima gwargwadon ikonsa.

Buhari ya bayyana haka ne a lokacin da ya kai gaisuwar ban girma ga mai martaba Sarkin Bauchi Alhaji Rilwanu Adamu a wani gangamin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC a Bauchi.

“A shekarar 2003 da 2012 na ziyarci daukacin kananan hukumomin kasar nan guda 774, kuma a shekarar 2019 da na sake tsayawa takara karo na biyu na ziyarci dukkan jihohin kasar nan.

“Don haka, a can na yi alkawari da alkawarin cewa zan bauta wa Najeriya da ‘yan Nijeriya iyakar iyawara,” inji shi.

Shugaban wanda ya kuma yabawa Sarkin bisa wannan tarba da aka yi masa, ya yabawa Gwamna Bala Mohammed kan yadda ake gudanar da ayyuka masu inganci a jihar.

Da yake mayar da martani, Adamu ya gode wa shugaban kasar bisa wannan ziyara, sannan ya bukaci ‘yan siyasa da su rika yin siyasa ba tare da dacin rai ba.

A yayin da ya yaba wa gwamnan bisa tabbatar da daidaito a tsakanin dukkanin jam’iyyun siyasar jihar, uban gidan sarautar ya yi addu’a tare da yi wa shugaban kasar fatan alheri.

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa shugaban ya samu rakiyar shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Adamu, shugaban majalisar dattawa, Ahmed Lawan, da kakakin majalisar wakilai, Femi Gbajabiamila.

Sauran sun hada da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC da abokin takararsa, Bola Tinubu da Kashim Shettima da dai sauransu.

legit ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp