Shugaban kasa Muhammadu Buhari a ranar Litinin din nan, ya ce, ya yi alkawarin yi wa ‘yan Najeriya hidima gwargwadon ikonsa.
Buhari ya bayyana haka ne a lokacin da ya kai gaisuwar ban girma ga mai martaba Sarkin Bauchi Alhaji Rilwanu Adamu a wani gangamin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC a Bauchi.
“A shekarar 2003 da 2012 na ziyarci daukacin kananan hukumomin kasar nan guda 774, kuma a shekarar 2019 da na sake tsayawa takara karo na biyu na ziyarci dukkan jihohin kasar nan.
“Don haka, a can na yi alkawari da alkawarin cewa zan bauta wa Najeriya da ‘yan Nijeriya iyakar iyawara,” inji shi.
Shugaban wanda ya kuma yabawa Sarkin bisa wannan tarba da aka yi masa, ya yabawa Gwamna Bala Mohammed kan yadda ake gudanar da ayyuka masu inganci a jihar.
Da yake mayar da martani, Adamu ya gode wa shugaban kasar bisa wannan ziyara, sannan ya bukaci ‘yan siyasa da su rika yin siyasa ba tare da dacin rai ba.
A yayin da ya yaba wa gwamnan bisa tabbatar da daidaito a tsakanin dukkanin jam’iyyun siyasar jihar, uban gidan sarautar ya yi addu’a tare da yi wa shugaban kasar fatan alheri.
Kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa shugaban ya samu rakiyar shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Adamu, shugaban majalisar dattawa, Ahmed Lawan, da kakakin majalisar wakilai, Femi Gbajabiamila.
Sauran sun hada da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC da abokin takararsa, Bola Tinubu da Kashim Shettima da dai sauransu.