Tsohon gwamnan jihar Kano, Dr. Rabi’u Kwankwaso ya fice daga jam’iyyar adawa ta PDP.
Murabus din Kwankwaso na kunshe ne a cikin wata wasika mai dauke da kwanan watan 29 ga watan Maris, kuma ya aike wa shugaban jam’iyyar PDP na gundumar sa.
Wani bangare na wasikar yana cewa: “Da zurfin tunani ne na rubuto don sanar da ku, cewa sakamakon wasu bambance-bambance masu tsanani da ba a daidaita su ba, na cimma matsayar cewa, ci gaba da zama a jam’iyyar PDP ba zai yu ba. A yau Talata 29 ga Maris, 2022, na janye takarara daga jam’iyyar PDP.”
Tsohon Sanatan ya kuma bayyana cewa zai koma jam’iyyar New Nigeria Peoples Party, NNPP a karshen watan Maris.