fidelitybank

Na yanke ‘ya’yan Marainana saboda na nesanta da mata – Bob Korna

Date:

Wani mutum a jihar Binuwe mai suna Terhemen Anongo ya yanke ’ya’yan marainansa biyu, domin gudun duniya da kuma kauce wa fadawa halaka.

Terhemen Anongo mai shekaru 44, wanda aka fi sani da ‘Doc K’ ko ‘Bob Korna’ a yankin Gboko na Jihar Binuwe, ya ce, a yanzu rayuwa ta fi masa dadi bayan wannan hukunci da ya yanke.

A wata hira da ya yi da Aminiya a Makurdi, babban birnin Jihar Binuwe, Anongo ya ce, ba haka siddan ya yanke ’ya’yan marainansa ba, sai dai ya yi hakan ne domin ya yi nesa-nesa da sha’awar ’ya’ya mata wanda hakan zai ba shi damar tsantsanta bauta ga Ubangijinsa ba tare da wani abu ya dauke masa hankali ba.

Tun a watan Maris na bara ne labarin Anongo ya bulla, a lokacin da ya yanke daya daga ’ya’yan marainansa da kansa wanda a sanadiyar haka ya kusa rasa ransa.

Sai dai bayanai sun ce, da yake yana da kwanaki a gaba, wasu kwararrun likitoci da suka yi masa rubdugu wajen fahimtar halin bukata da yake ciki suka ceto ransa ta hanyar yi masa tiyata bayan ya yi asarar jini mai tarin yawa.

A ranar Litinin ta makon da ya gabata ce, Anongo ya yanke dan marainansa na biyun, inda ya sake nanata cewa, hakan zai ba shi damar tsantsanta bauta ga Ubangijinsa ba tare da mata sun dauke masa hankali ba.

Tarihi dai ya nuna cewa, tun a aji na biyar Anongo ya yi watsi da karatun likitanci da yake yi a Jami’ar Ibadan, inda ya koma mai tura baro a yankin na Gboko.

“Na shiga Jami’ar Ibadan a shekarar 1996, kuma a shekarar 2000 har na ci jarrabawar da za mu tafi Asibitin Koyarwa na Jamiar domin karbar horo a kan makamar aiki, sai na yanke shawarar watsi da karatun saboda matsananciyar damuwa da nake fama da ita.

“A lokacin na daina sha’awar karatun gaba daya, sai dai kuma daga baya na yi kokarin komawa karatun amma mahukuntan jami’ar suka ce da ni ai ta faru ta kare.

“Na yanke dan marainan nawa na farko a ranar 10 ga watan Janairun 2021, sai dai an samu tangarda domin kuwa kwayoyin cututtuka sun shiga jikina, amma hakan bai hana na ci gaba da gudanar da harkokina ba har zuwa lokacin da na warke kuma yanzu garau nake don babu abin da ke damu na.

“A wancan lokaci ina aiki ne a wani Kamfanin Sufuri da ake kira Flight, amma sai suka sauya tsare-tsarensu na gudanarwa, wanda hakan ya sanya na ajiye musu aikinsu.

“A halin yanzu ina rayuwa ta cikin annashuwa da jin dadi kasancewar ina abokai masu kirki da suka rika kula da ni, akwai yan uwana mata da suka rika aiko min da abun alheri lokaci bayan lokaci.

“Na ajiye kayan abinci da dama a gidana, kuma duk lokacin da nake da wata bukata na kan tashi na girka da kaina. Na kuma rika biyan mutanen da suka kula da ni asibiti. A cewar Bob Korna.

daily post nigeria today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Yadda aka gudanar da addu’o’in Buhari a Villa

A ranar Alhamis ne aka gudanar da addu'o'i ga...

Rasha tarnaki ce a wajen Tarayyar Turai – Jamus

Shugaban gwamnatin Jamus Friedrich Merz ya shaidawa BBC cewa...

Amurka ba ta goyon bayan Isra’ila a harin Syria – Trump

Amurka ta ce ba ta goyon bayan hare-haren da...

Tinubu zai zo Kano ta’aziyyar Dantata

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu zai kai ziyara Kano yau...

Tarayyar Turai tamince da ƙaƙaba wa Rasha sabbin takunkumai

Ƙungiyar Tarayyar Turai ta amince da ƙaƙaba wa Rasha...

Gwamnan Filato ya zargi Jami’ai da kin kama ‘yan bindiga

Gwamnatin jihar Filato ta zargi jami'an sojojin ƙasar da...

Za a yi wa Buhari addu’a a Abuja

Gwamnatin Tarayya za ta jagoranci gudanar da taron addu'o'i...

Buhari ya ban umarni na kula da Talakawan Najeriya – Peter Obi

Jagorar jam'iyyar LP a Najeriya, Peter Obi ya ce,...

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...

Shettima ya jagoranci yi wa Buhari addu’o’i na musamman a Daura

An gudanar da addu'o'i na musamman don neman gafara...

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...
X whatsapp