fidelitybank

Na yabawa Obi bisa zabar Dan Achaba a matsayin dan majalisa – Omokri

Date:

Mai fafutuka, Reno Omokri ya yabawa jam’iyyar Labour Party da dan takararta na shugaban kasa, Peter Obi bisa zabar dan Achaba wato Okada, Donatus Mathew a matsayin wakilin mazabar Kaura na Kudancin Kaduna.

Idan za a iya tunawa dai an bayyana dan takarar jam’iyyar Labour ne a matsayin wanda ya lashe zaben bayan ya samu kuri’u 10,466 inda ya doke jam’iyyar APC mai mulki da ta samu kuri’u 9,828.

A nasa jawabin Omokri, dan takarar jam’iyyar PDP a zaben da aka kammala, Atiku Abubakar ya bayyana zaben Mathew a matsayin dimokradiyya ta gaskiya.

A wani sako da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Omokri ya bayyana kwarin guiwar fitowar dan takarar jam’iyyar LP a matsayin wanda ya lashe zaben zai janyo karin magoya bayan jam’iyyar a arewacin kasar.

Ya rubuta cewa, “A karkashin jam’iyyar Labour, wani dan tseren Okada, Donatus Mathew, ya lashe zaben majalisar wakilai a Kaduna. Wannan ita ce dimokuradiyya a cikin mafi kyawun tsarinta. Kuma saboda wannan, na gode wa Peter Obi da Jam’iyyar Labour.

“Dukansu biyu sun yi kokari sosai wajen zurfafa dimokuradiyyarmu. Ban taba tunanin hakan zai iya faruwa a Najeriya a shekara ta 2923. Nan gaba watakila na yi tunanin hakan zai faru. Amma ba yanzu ba.

“Idan har kungiyar kwadago ta ci gaba da haka, za su sa Najeriya ta zama al’umma mai daidaito.

“Wannan labarin zai kara samun karbuwa a Kano, cibiyar tabbatar da daidaito a Arewacin kasar, wanda shine manufa ta utopian da marigayi Aminu Kanu ya yi kokarin ginawa tare da Talakawa ta hanyar Northern Elements Progressive Union, daga baya kuma jam’iyyarsa ta Peoples Redemption Party”.

www.legit news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp