fidelitybank

Na tsallake rijiya da baya lokacin Goodluck – Shettima

Date:

Mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima ya ce shi ne mutumin da aka fi ”ɓata wa suna” a lokacin mulkin tsohon shugaban ƙasar Goodluck Jonathan.

Yayin da yake jawabi a lokacin ƙaddamar a littafin tsohon ministan shari’ar ƙasar, Mohammed Bello Adoke da aka gudanar a Abuja ranar Alhamis, Shettima ya ce Jonathan ya taɓa kawo shawarar cire shi daga muƙaminsa na gwamnan jihar Borno.

Amma sai tsohon ministan ƙasar, kuma babban lauyan gwamnati, Mohammed Bello Adoke ya ba shi shawarar kauce wa yin hakan.

Shettima ya ce Adoke ya nuna jarumta wajen faɗa wa Jonathan cewa kundin tsarin mulki bai ba shi damar cire ko da zaɓaɓɓen kansila, balle gwamna sukutum.

Kawo yanzu dai tsohon shugaban ƙasar, GoodLuck Jonathan bai mayar da martani dangane da iƙirarin na Kashim Shettima ba.

A watan Mayun 2013 ne Jonathan ya ayyana dokar ta ɓaci kan jihohin da ke fama da rikicn Boko Haram da suka haɗa da Borno da Yobe da kuma Adamawa, to amma bai dakatar da gwamnonin ba.

Kashim Shettima ne gwamnan jihar Borno har tsawon wa’adi biyu, daga 2011 zuwa 2019, kuma ya mulki jihar a daidai lokacin da rikicin Boko Haram ya munana a yankunan arewa maso gabashin Najeriya.

mmm.nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya ba za ta karbi ‘yan ciranin Venezuela ba da Amurka za ta ba mu – Najeriya

Ministan harkokin wajen Najeriya, Yusuf Tuggar ya ce ƙasar...

Bafarawa ya kafa sabuwar kungiya

Wasu shugabanni da sauran masu ruwa da tsaki daga...

An fara shirye-shiryen aikin Hajjin badi a Najeriya

Hukumar Alhazan Najeriya ta fara shirhin aikin hajjin 2026...

Na tsallake rijiya da baya lokacin Goodluck – Shettima

Mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima ya ce shi ne...

Ya kamata shugabancin Najeriya ya ci gaba da zama a hannun ƴan Kudu

Ministar al'adu ta Najeriya, Hannatu Musawa ta ce ya...

Rashin abinci mai gina jiki Najeriya ce kan gaba a Afirka ta biyu a duniya

Babbar mai taimaka wa shugaban Najeriya Bola Tinubu kan...

Gwamnatin Najeriya ta ciyo bashin dala miliyan 747

Najeriya ta karɓo bashin dala miliyan 747 daga bankunan...

Ba don Tinubu ba ko zaɓen fitar da gwani Buhari ba zai ci ba

Babban mai taimaka wa Shugaba Tinubu kan kafofin yaɗa...

Majalisa ta gayyaci Gwamnan Filato kan tsaron jihar

Kwamitin wucin gadi kan matsalolin tsaron jihar Filato na...

Sojoji sun sun kashe ‘yan Boko Haram 24

Rundunar Sojoji ƙarƙashin rundunar 'Operation Hadin Kai' mai yaƙi...

Dangote zai gina rumbum man fetur da dizel a Namibia

Matatar mai ta Dangote da ke Najeriya za ta...

Dangote ya rage farashin litar mai zuwa ₦820

Kamfanin matatar man Dangote ya rage farashin litar mai...
X whatsapp