fidelitybank

Na tsallake rijiya da baya lokacin Goodluck – Shettima

Date:

Mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima ya ce shi ne mutumin da aka fi ”ɓata wa suna” a lokacin mulkin tsohon shugaban ƙasar Goodluck Jonathan.

Yayin da yake jawabi a lokacin ƙaddamar a littafin tsohon ministan shari’ar ƙasar, Mohammed Bello Adoke da aka gudanar a Abuja ranar Alhamis, Shettima ya ce Jonathan ya taɓa kawo shawarar cire shi daga muƙaminsa na gwamnan jihar Borno.

Amma sai tsohon ministan ƙasar, kuma babban lauyan gwamnati, Mohammed Bello Adoke ya ba shi shawarar kauce wa yin hakan.

Shettima ya ce Adoke ya nuna jarumta wajen faɗa wa Jonathan cewa kundin tsarin mulki bai ba shi damar cire ko da zaɓaɓɓen kansila, balle gwamna sukutum.

Kawo yanzu dai tsohon shugaban ƙasar, GoodLuck Jonathan bai mayar da martani dangane da iƙirarin na Kashim Shettima ba.

A watan Mayun 2013 ne Jonathan ya ayyana dokar ta ɓaci kan jihohin da ke fama da rikicn Boko Haram da suka haɗa da Borno da Yobe da kuma Adamawa, to amma bai dakatar da gwamnonin ba.

Kashim Shettima ne gwamnan jihar Borno har tsawon wa’adi biyu, daga 2011 zuwa 2019, kuma ya mulki jihar a daidai lokacin da rikicin Boko Haram ya munana a yankunan arewa maso gabashin Najeriya.

nnnhausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp