Tsohon kocin Super Eagles, Gernot Rohr ya bayyana cewa, yayi kokarin shawo kan matashin dan wasan Bayern Munich Jamal Musiala ya bugawa Najeriya wasa.
An haifi Musiala a kasar Jamus ga mahaifin dan Najeriya kuma mahaifiyar Birtaniya.
Dan wasan ya zabi ya wakilci Jamus a matakin manya bayan ya fara bugawa Ingila wasa a matakin matakin shekaru.
Rohr, wanda ya jagoranci Super Eagles tsakanin 2016 zuwa 2021 ya bayyana cewa ya yi kokarin shawo kan dan wasan mai shekaru 19 ya wakilci zakarun Afirka sau uku.
Rohr ya shaida wa Owngoal cewa “Ina fata da na samu Musiala ya buga wa Najeriya wasa, amma ya zabi ya buga wa Jamus wasa.”
“Dan wasa ne mai ban sha’awa, na sadu da shi lokacin yana shekara 17, kuma na yi magana da wakilansa da iyayensa.
“A wannan lokacin, ya kasa yanke shawara, kuma bayan shekara guda, ya zama abin da yake yanzu, kuma shi ke nan.”
Hukumar kwallon kafa ta Najeriya ta kori Rohr a watan Disambar 2021.