fidelitybank

Na shirya jagorantar gamayyar jam’iyyun adawa domin tiƙa Tinubu da ƙasa a 2027 – Atiku

Date:

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) a zaben 2023, Atiku Abubakar, ya bayyana cewa a shirye yake ya jagoranci gamayyar jam’iyyun adawa don kawar da jam’iyyar All Progressives Congress (APC) mai mulki a 2027.

Atiku ya bayyana hakan ne a sakon taya murna ga gwamnonin jam’iyyar PDP, wadanda kotun koli ta amince da zabensu a ranar Juma’a.

A wata sanarwa mai dauke da sa hannun ofishin yada labarai a Abuja, Atiku ya bayyana hukuncin kotun a matsayin albishir ga al’ummar jihohin Bauchi da Filato da Kuros Riba da kuma Zamfara, kuma hakika nasara ce ga tsarin mulkin dimokradiyya.

Ya kuma jaddada matsayinsa na cewa hadin kan ‘yan adawa ne kadai zai iya karfafa dimokradiyya a Najeriya.

An jiyo Atiku yana cewa, “Ni a shirye nake kamar yadda aka saba, domin in jagoranci wannan mukami, tare da dukkan shugabanninmu da Gwamnoninmu, domin ci gaban kasarmu.”

A cewarsa, “Inda aka ga an yi adalci sosai, mu a matsayinmu na masu kishin kasa da kuma ‘yan kasa, za mu yaba.”

Hakazalika Atiku ya ce bisa hukuncin kotun koli, “akwai tabbacin ci gaba da tsare-tsaren shugabanci nagari da PDP ta kawo a jihohinsu.”

Ya yi kira ga gwamnonin PDP, wato: Bala Mohammed na Bauchi, Dauda Lawal na Zamfara, Barr. Caleb Muftwang na Filato da Fasto Umo Eno na Akwa Ibom don ganin nasarar da suka samu a kotun koli a matsayin wata dama ce ta karfafa tare da fadada fa’idar shugabanci nagari da suka riga suka kafa.

latest news in nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp