Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya ce, gwamnatinsa ta kashe sama da dala biliyan daya wajen sayen kayan aikin soji domin kwato yankunan Arewa maso Gabas da Boko Haram ta kama.
Femi Adesina, mai ba Buhari shawara na musamman kan harkokin yada labarai da wayar da kan jama’a ne ya bayyana hakan a ranar Talata.
A cewar sanarwar, taron zaman lafiya na Abu Dhabi ne ya karrama Buhari da lambar yabo don karfafa zaman lafiya a Afirka.
A cikin jawabinsa a taron zaman lafiya na Afirka 2023 a Mauritania, Buhari ya bayyana cewa Afirka da sauran kasashen duniya suna aiki tukuru don magance barazanar wanzuwar bil’adama.
“Lokacin da na zama shugaban kasa a shekarar 2015, Boko Haram sun rike kusan kashi biyu bisa uku na jihar Borno, rabin jihar Yobe, da kuma wasu kananan hukumomi biyu a jihar Adamawa, duk a Arewa maso Gabashin Najeriya.
“Mun sami damar maido da wadannan yankuna ta hanyar zuba jari fiye da dala biliyan 1 don samun makamai masu karfi da software daga Amurka da sauran kasashen abokantaka don gudanar da ayyukan ci gaba da yaki da ta’addanci tun 2015.”