Shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, ya miƙa saƙon jajen sa ga mutuwar sojojin Najeriya biyu, wadanda suka yi hatsarin jirgin saman soji a jihar Kaduna.
A wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasar, Mallam Garba Shehu, ya fitar ya ce, Shugaba Buhari yana bayyana damuwarsa, bisa mutuwar Flight Laftanar Abubakar Alkali da Flight Laftanar Elijah Haruna Karatu.
“Na yi matukar kaduwar da ba zan iya cewa komai ba bisa rasuwar wadannan matasa biyu wadanda suka sadaukar da rayuwar wajne bauta wa kasa,” in ji Buhari.
Ranar Talata ne jirgin rundunar sojin sama ta Najeriya ya yi hatsari inda duka jami’an biyu da ke cikinsa suka mutu.
A cikin shekara guda da ta gabata dai, jiragen sojin saman Najeriya na yawan faduwa, lamarin da ke sanadiyar mutuwar jami’an sojin.