zababben shugaban kasa, Bola Tinubu, ya yabawa ɗan wasan dambe, Isra’ila Adesanya kan sake samun kambun UFC 287 na matsakaicin nauyi.
Adesanya ya yi kaca-kaca da abokin karawarsa, Alex Pereira, sannan ya dawo da kambun UFC 287 na matsakaicin nauyi a gasar da aka gudanar a birnin Miami na kasar Amurka.
Alkalan fada na UFC Middleweight ya nuna cewa Pereira ya samu maki 7 – 2 – 0 a kan Adesanya wanda ya koma gida da maki 24 – 2 – 0 bayan fafatawar daren Asabar.
Idan dai za a iya tunawa Adesanya ya yi yunkurin farko, inda ya ci gaba da zama zakaran UFC har zuwa lokacin da ya rasa belinsa a hannun Pereira a haduwarsu ta farko ta MMA, watanni biyar da suka gabata.
A wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter a ranar Lahadi, Tinubu ya ce, Adesanya bai daina yarda da kansa ba kan kwato kambun UFC na matsakaicin nauyi.
Zababben shugaban kasar ya kuma bayyana cewa ‘yan Najeriya ba su daina yarda da shi ba da kuma sanya kasar alfahari.