Gwamna Hope Uzodinma na jihar Imo ya ce, wasu dake jikin shugaban kasa Bola Tinubu wanda ake kira Kabal da ke cin gajiyar arzikin kasar nan ke ɗaukar nauyin zanga-zangar matasa.
Uzodinma ya ce ‘yan jam’iyyar su ne suka dauki nauyin zanga-zangar da ake yi a fadin kasar nan na nuna adawa da Tinubu duk da cin gajiyar arzikin Najeriya.
A wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a, gwamnan ya kuma yabawa al’ummar yankin Kudu maso Gabas da rashin shiga zanga-zangar da aka yi a fadin kasar.
Da yake lura da cewa zanga-zangar lumana hakki ne na ‘yan kasa, Uzodinma ya jaddada cewa Tinubu ya nuna jajircewarsa wajen tunkarar kalubalen da kasar ke fuskanta.
A cewar gwamnan: “Ina yaba wa al’ummarmu na yankin Kudu maso Gabas da suka yi biyayya ga kiran da muka yi na kada su shiga zanga-zangar da ake yi a fadin kasar nan. Hikimar ku na sanin haɗarin da masu satar mutane ke yi wa masu zanga-zangar lumana abin a yaba ne da gaske.
“Yayin da zanga-zangar lumana ba shakka hakki ne na mutane, shawarar da kuka yanke na ba da fifiko ga aminci da kwanciyar hankali yana nuna taka tsantsan.
“Abin takaici ne cewa wadanda suka bayar da gudunmawa wajen kalubalen tattalin arzikin da muke fama da su a halin yanzu su ne ke daukar nauyin zanga-zangar maimakon yin aiki da FG don warware matsalar.
“Wannan martanin ya zo ne kawai saboda muna da Shugaban kasa wanda ke da karfin gwiwa don wargaza baragurbin da ke cin gajiyar albarkatunmu.”