Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC), Asiwaju Bola Tinubu, a ranar Lahadi, ya ce, shi da tawagarsa sun yi farin ciki lokacin da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da bukatar kara wa’adin tsohuwar takardar naira.
Tinubu ya bayyana haka ne a lokacin yakin neman zabensa a garin Benin na jihar Edo, inda ya gudanar da wani taro na gari da shugabannin siyasa, kungiyoyin al’umma da kwararru daga sassa daban-daban.
Ya ce, “Mun yi kwana uku zuwa hudu a kan haka, kwatsam yau, da Shugaban kasa ya ce lafiya saboda mutuntawa zai yi la’akari da bukatar da muka yi ta neman karin wa’adin, mun ji dadi.