Gwamna Atiku Bagudu ya ce a shirye ya ke ya mika wa Sanata Adamu Aliero, kujerar majalisar da ke wakiltar yankin a majalisar wakilai ta kasa tikitin takarar jamâiyyar All Progressives Congress (APC) na shiyyar Kebbi ta tsakiya idan har akwai bukatar yin hakan.
Gwamnan jihar Kebbi ya yi magana ne bayan an bayyana shi a matsayin wanda ya lashe tikitin takarar Sanata na jamâiyyar APC ta Kebbi ta tsakiya a jamâiyyar APC, a sakamakon zaben fidda gwani da aka gudanar a Sakatariyar Haliru Abdu da ke Birnin Kebbi, babban birnin jihar.
Kamfanin Dillancin Labarai na Ĉasa, NAN, ya rawaito cewa Sanata Adamu Aliero, wanda ke neman tikitin takara ya janye daga takarar wasu saâoâi kafin a fara zaben fidda gwani.