Dan takarar jam’iyyar Labour a mazabar Ibarapa ta gabas a zaben gwamna da na ‘yan majalisar jiha a jihar Oyo, Hon Adesope Abiodun ya janye aniyarsa.
Abiodun ya bayyana cewa ya janye takararsa ga shugaban majalisar dokokin jihar Oyo, Adebo Ogundoyin.
Ya bayyana hakan ne a karshen wata ganawa da shugaban majalisar da shugabannin jam’iyyar PDP a karamar hukumar Ibarapa ta Gabas.
Karanta Wannan: INEC na amfani da karfin tuwo ga wasu mutane – Dan Takarar Gwamnan NNPP
Abiodun, wanda ya yi magana a taron da aka gudanar a karshen mako, ya yi alkawarin yin aiki domin samun nasarar shugaban majalisar a zaben da aka yi a ranar Asabar 18 ga watan Maris na wannan shekara.
Ya ci gaba da cewa magoya bayan jam’iyyar Labour Party da mambobinta a dukkan sassan mazabu da mazabar za su hada kai da jam’iyyar PDP don ganin nasarar Gwamna Seyi Makinde.
Ya ce, “Na yi farin cikin bayyana goyon bayana ga Hon Adebo Ogundoyin. Kuma ina so in ce jam’iyyar Labour Party, LP, a Ibarapa East a shirye take ta ba dan takarar PDP goyon baya a zabe mai zuwa. Wannan shawara ce gama gari”.
Ita ma kungiyar Allied People’s Movement (APM) a karamar hukumar Ibarapa ta gabas ta yi alkawarin marawa shugaban majalisar baya.
Dan takarar jam’iyyar APM mai wakiltar mazabar Ibarapa ta gabas/Ido a zaben majalisar tarayya da ya gabata, Honarabul Opeyemi Ayanrinde ya bayyana hakan a karshen mako.