Babban Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami, SAN, ya ce, janyewar da ya yi daga takarar Gwamnan Jihar Kebbi a kwanakin baya, ya samo asali ne saboda kishin kasa kuma ya cancanci a yaba wa ‘yan Najeriya.
Malami, wanda ya yi magana ta bakin mai magana da yawunsa, Dakta Umar Gwandu ya ci gaba da cewa, bai taka wata doka da wannan mataki ya dauka ba, domin hakkinsa ne na dayansa ya zabi ya janye aniyarsa ta siyasa da kan sa.
A wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, Gwandu ya ce Malami bai yi murabus daga mukaminsa na AGF ba, duk da halartar bikin karramawar da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya shirya, inda ya kara da cewa, lamari ne da ya shafi shari’a da hakkinsa wanda bai taka wata doka ba.
Ya kuma kara da cewa masu tunani na gaskiya na al’umma suna mutunta hakkin daidaikun mutane na yancin zabi a cikin al’amuran da suka shafi wannan.
Idan dai za a iya tunawa, a ranar 28 ga watan Afrilu ne AGF ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar gwamnan jihar Kebbi a wani taron masu ruwa da tsaki a Birnin Kebbi.