fidelitybank

Na hango tashin Bam a gasar cin kofin AFCON – Malamain Majami’a

Date:

Wani malamin majami’a, Nigel Gaisie  ya yi gargadi game da harin ta’addanci a lokacin gasar cin kofin nahiyar Afirka, AFCON, da za a fata a Kamaru.

Gaisie ya bayyana cewa ya hango ‘yan ta’adda sun tayar da bama-bamai a wani filin wasa a lokacin gudanar da gasar AFCON.

Da ya ke jawabi ga mambobinsa, malamain dan kasar Ghana ya bukaci kasashen da ke halartar gasar da su yi addu’a, domin kaucewa bala’i a lokacin gasar da za a yi a kasar Kamaru.

A cewar Gaisie: “Wannan annabci ne na duniya. Ubangiji ya dauki ruhina zuwa wuri kamar Kamaru game da gasar cin kofin Afirka na 2021.

“Na ga wani abu kamar ‘yan wasa a tsaye a kan gado kuma suna jin zafi yayin da wasu daga cikinsu ke kuka.

“Bari al’ummar Kamaru su yi addu’a da duk wata tawagar da ta cancanta su yi haka, domin ina ganin wani abu kamar harin ta’addanci da hare-haren bama-bamai.

“Ina ganin cewa wani abu ya faru a filin wasa kuma duk wurin ya kasance cikin rikici kuma mutane sun mutu.” Inji Gaise.

DAILY POST ta rawaito cewa,  gwamnatin Ghana ta gargadi fastoci game da fitar da annabce-annabce da za su haifar da firgici da fargaba.

A ranar Lahadi 9 ga watan Janairu, 2022 za a fara gasar AFCON ta shekarar 2021 a kasar Kamaru.

A halin da a ke ciki dai kungiyar Super Eagles ta Najeriya ta isa kasar Kamaru gabanin fara gasar.

 

vanguard newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...
X whatsapp