Wani malamin majami’a, Nigel Gaisie ya yi gargadi game da harin ta’addanci a lokacin gasar cin kofin nahiyar Afirka, AFCON, da za a fata a Kamaru.
Gaisie ya bayyana cewa ya hango ‘yan ta’adda sun tayar da bama-bamai a wani filin wasa a lokacin gudanar da gasar AFCON.
Da ya ke jawabi ga mambobinsa, malamain dan kasar Ghana ya bukaci kasashen da ke halartar gasar da su yi addu’a, domin kaucewa bala’i a lokacin gasar da za a yi a kasar Kamaru.
A cewar Gaisie: “Wannan annabci ne na duniya. Ubangiji ya dauki ruhina zuwa wuri kamar Kamaru game da gasar cin kofin Afirka na 2021.
“Na ga wani abu kamar ‘yan wasa a tsaye a kan gado kuma suna jin zafi yayin da wasu daga cikinsu ke kuka.
“Bari al’ummar Kamaru su yi addu’a da duk wata tawagar da ta cancanta su yi haka, domin ina ganin wani abu kamar harin ta’addanci da hare-haren bama-bamai.
“Ina ganin cewa wani abu ya faru a filin wasa kuma duk wurin ya kasance cikin rikici kuma mutane sun mutu.” Inji Gaise.
DAILY POST ta rawaito cewa, gwamnatin Ghana ta gargadi fastoci game da fitar da annabce-annabce da za su haifar da firgici da fargaba.
A ranar Lahadi 9 ga watan Janairu, 2022 za a fara gasar AFCON ta shekarar 2021 a kasar Kamaru.
A halin da a ke ciki dai kungiyar Super Eagles ta Najeriya ta isa kasar Kamaru gabanin fara gasar.