Gwamnan jihar Rivers, Nyesom Wike, ya bayyana cewa shi ne mutumin da ya fi kowa cancanta ya mulki Najeriya a shekarar 2023.
Gwamnan, wanda ya yi magana a wata hira da gidan Talabijin na Channels, ya ce, babu wani dan Najeriya da ya ke da gogewar da zai shugabanci Najeriya.
A cewar Wike, kasancewarsa Minista da kuma gwamnan jihar mai arzikin man fetur ya ba shi kwarewar da ake bukata wajen tafiyar da mulkin kasar.
Ya ce, “Da a ce yau ina son tsayawa takarar shugaban kasa, wane irin inganci ku ke ganin bani da shi? Me ya sa ku ke ganin ba zan iya samar da ingantaccen shugabanci ga Najeriya domin ci gaba ba? . In ji Wike.