fidelitybank

Na fi kowa cancanta a takarar shugaban ƙasa a PDP – Tambuwal

Date:

Aminu Waziri Tambuwal ya bukaci jam’iyyar PDP da ta tattara ayyukanta, ta kuma matsa kaimi wajen ganin ta fito da dan takarar shugaban kasa da ‘yan Najeriya za su kasance a shirye su mara masa baya a zaben 2023.

Dan takarar shugaban kasar dai, ya ce yana da dukkan abubuwan da ake bukata, domin cika sharuddan da ‘yan Najeriya ke nema.

Tambuwal ya bayyana haka ne a yammacin Larabar da ta gabata a lokacin da ya gana da taron tsaffin ministocin tarayyar Najeriya karkashin jam’iyyar PDP a Asokoro, Abuja.

“Abin da ke da mahimmanci ga PDP shi ne dan takara da za mu iya yin aiki tare, don kai mu ga ci wannan zabe, ba daga inda mutum ya fito ba,” Gwamnan Sokoto ya shaida wa tsoffin shugabannin kasar.

Da yake bayyana cewa, son kai da kishin kasa da hadin kan al’ummar kasar ne ke neman sa na neman babban mukami a kasar, ya ce “ba wani abu ba ne na kashin kai. Ya shafi kasarmu gaba daya.”

Da yake magana shaidarsa na uku wanda ya rataya a kan bangaren zartarwa, majalisa, da shari’a, ya jaddada cewa yana da kyakkyawar fahimtar kasar, inda, abin takaici, “abubuwa suna kara tabarbarewa.”

legit news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...
X whatsapp