Muƙaddashin babban hafsan sojin ƙasar nan, Laftanar Janar Olufemi Oluyede, ya sha alwashin tabbatar da zaman lafiya mai ɗaurewa a Najeriya idan aka tabbatar masa da muƙamin shugabancin shugabancin rundunar sojin ƙasan ƙasar.
Ya bayyana hakan ne a lokacin da ya bayyana a gaban kwaminitin tsaro na majalisar wakilai ta Najeriya a ranar Laraba, kamar yadda shafin intanet na tashar Chanells ya ruwaito.
Ya ce matsalar tsaron Najeriya a yanzu na buƙatar haɗin kai daga dukkan masu ruwa da tsaki domin tabbatar da zaman lafiya a lungu da saƙon ƙasar.
Ya ce, “a sama da shekara 30 da na yi ina aikin soja, na yi aiki a wurare daban-daban a rundunar sojin ƙasan Najeriya. Don haka ba zan tsame hannuna daga dukkan nasarori ko rashinsa da aka samu a baya ba, amma idan aka tabbatar da ni, zan samu wata dama jan ragamar rundunar tare da kawo wasu dabarun da za su taimaka domin rundunar ta samu ƙarin nasarori.”