fidelitybank

Mutuwar Sarki: Kuwait ta bayar da hutun kwana 40 tare da sauran kasashe

Date:

Ƙasar Kuwait ta ayyana hutun kwana 40 domin alhini da jimamin mutuwar Sarkin Kuwait Sheikh Nawaf Al-Ahmad Al-Jaber Al-Sabah.

Ministan da ke kula da harkokin majalisar zartarwa ta ƙasar ne ya sanar da hakan, sannan kuma an rufe duk wasu wuraren aiki har na tsawon kwana uku.

A wani mataki na nuna alhini daga ƙasashen Larabawa game da mutuwar Sarkin Kuwait Sheikh Nawaf Al-Ahmad Al-Jaber Al-Sabah, ƙasashen Masar da Lebanon da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa sun ayyana hutun kwana uku domin alhini.

Bayan ga hutun kwanaki ukun an kuma sassauta tutoci ƙasa a duka ofisoshin ƙasar da na jakadanci a duka ƙasashen, kuma za a fara makokin ne daga ranar Asabar.

Wannan dai gagarumin rashi ne da aka yi ga duniyar larabawa wanda kuma za a dade ana jimami.

Allah ya yi wa Sarki Kuwait Sheikh Nawaf al-Ahmad al-Jaber al-Sabah rasuwa yana da shekara 86 a duniya.

Sheik shi ya jagoranci ƙasar mai arziƙin man fetur na tsawon shekaru uku da suka gabata bayan karɓar jagorancin ƙasar daga ɗan uwansa Sheikh Sabah al-Ahmed al-Sabah.

“Cikin baƙin ciki da juyayi, muna makokin… mutuwar Sheikh Nawaf al-Ahmad al-Sabah” cikin wata sanarwa da aka karanta a gidan talabijin na ƙasar.

An naɗa Sheikh Nawaf a matsayin yarima mai jiran gado a 2006 kuma a 2020 ya zama sarki.

A baya ya taɓa rike muƙamin ministan tsaro da harkokin cikin gida.

Kuwait wadda ke da yawan mutane da suka kai miliyan 4.8 ciki har da ‘yan ƙasashen waje miliyan 3.4 da ke aiki a ƙasar – ita ce ta shida a jerin ƙasasheb masu arziƙin mai kuma tana cikin manyan ƙawayen Amurka.

legit.ng.news.

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp