Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce, matsalar mutuwar mata lokacin haihuwa a jihohin arewa ta tsakiya ciki har da Neja, ba ta raguwa saboda matsalar tsaro, duk da ƙoƙarin da jami’ai ke yi.
Hukumar ta ce da yawan yaran da aka haifa a yankin ba a yi masu riga-kafi ba, saboda yawan rikicin da ake samu masu alaƙa da rashin tsaro.
Shugabar da ke kula da shiyyar, Dr Asma’i Zeenat Kabir ce ta bayyana hakan a taron WHO na 75 da ya gudana a Minna babban birnin Neja.
Ta ƙara da cewa har yanzu akwai gagarumin ƙalubale a ɓangaren haihuwa da mutuwa, da kuma a lokacin haihuwa da wasu matsaloli masu alaƙa da yara a mafi yawan jihohin yankin.
Don haka akwai buƙatar sake zage damtse don bunƙasa harkokin lafiya a yankin.