fidelitybank

Mutuwar Magoya Baya: ‘Yan sandan Tunusiya sun samu gurbi a gidan yari

Date:

Kotu a Tunisiya ta ɗaure ‘yan sanndan ƙasar shekara biyu a gidan yari saboda mutuwar wani magoyin bayan ƙwallon ƙafa.

Omar Laabidi mai shekara 19 ya nitse a ruwa a 2018 lokacin da yake yunƙurin tsira daga ‘yan sandan da suka biyo wani gungun magoya bayan ƙwallon ƙafa a gefen wata ƙorama.

An ruwaito cewa Laabidi ya yi ta ihun cewa ba zai iya ninƙaya ba kafin daga baya ya afka cikin ruwan don guje wa ‘yan sandan. Washegari aka fito da gawar Laabidi.

Shaidu sun ce sun ji ‘yan sanda na yi masa tsawa cewa “dole ka san yadda za ka yi ninƙaya”, abin da ya zama abin faɗa a shafukan zumunta maƙale da maudu’in #ApprendsÀNage daga mutanen da ke kiraye-kirayen a bi masa haƙƙinsa.

‘Yan uwan mamacin sun ce za su ɗaukaka ƙara kan hukuncin saboda abin da suka ce “ba cikakken adalci ba ne”.

daily sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp