Ɗan takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar PDP kuma gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, ya dage cewa, ba zai sauka daga takarar shugaban kasa a 2023 ba.
Wasu jiga-jigan jam’iyyar sun bukaci a zabi dan takarar shugaban kasa ta hanyar yarjejeniya.
Sai dai a wata hira da BBC Pigin, Wike ya ce, masu tunanin za su iya yaudare shi da irin wannan to su halakar da tunanin su.
Ya ce mutuwa ce kawai za ta iya sa shi ya ƙi tsayawa takara a zaben shugaban kasa na 2023.
“Me yasa zan sauka don kowa? Idan kuna son yin yarjejeniya, dole ne a sami daidaito da adalci. Hannun masu neman yarjejeniya suna da tsabta? Mutanen da ke magana a kan yarjejeniya su ne masu gudanar da zaben. Shin hukuncin jam’iyyar ne?”
“Ba jam’iyyar ce ke magana ba. A siyasa akwai abin da ake kira shine shine bobo. Da yawa ka duba, kadan ka gani. Wasu suna ganin za su iya yaudare ni da yarjejeniya. Yana da zamba. Ba na son a yaudare ni a rayuwata.”