Mutum guda ya mutu yayin da fiye da 30 suka nutse bayan wani kwale-kwale ɗauke da mutane ya kife a kogin Dundaye a ƙaramar hukumar Wamakko da ke jihar Sokoto.
Lamarin ya faru ne ranar Lahadi da safe, lokacin da mutanen suka shiga kwale-kwalen domin zuwa gonakinsu.
Shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa ta NEMA mai lura da jahohin Sokoto da Kebbi da Zamfara, Aliyu Shehu-Kafindangiya, ya tabbatar wa da BBC aukuwar lamarin, inda ya ce, jami’an hukumar da gwanayen ninƙaya a ruwa na ƙoƙarin ceto sauran fasinjojin da ba a gani ba.
”Lamarin ya faru da misalin ƙarfe 10:00 na safe, kuma mun zo da jami’anmu da kuma gwanayen nutso a ruwa domin a san yadda za a ceto waɗannan mutanen da ke cikin ruwa, yanzu dai an fiddo gawa guda kuma an wuce da shi gida domin a yi masa sutura kamar yadda addini ya tanada”, in ji jami’in hukumar NEMA, Aliyu Shehu-Kafindangi.
Matuƙin kwale-kwale wanda shi kaɗai ne da ya tsira, ya shaida wa BBC cewa suna kan hanyarsu ne daga garin na Dundaye zuwa fadama domin aikin shinkafa lokacin da lamarin ya faru.
Wannan na zuwa ne ‘yan kwanaki bayan wani kwale-kwale ɗauke da fasinjoji aƙalla 20 ya kife a jihar Jigawa, lamarin da ya janyo mutuwar aƙalla mutum 15.
Hatsarin kwale-kwale a Najeriya, wani abu ne da ke neman zama babban bala’i, wanda masana ke dangantawa da rashin ingancin jiragen da kuma ƙazamin lodi da ake yi wa kwale-kwalen.