fidelitybank

Mutun ɗaya ya mutu yayin da kwale-kwale ya kutse da mutane sittin a Sokoto

Date:

Mutum guda ya mutu yayin da fiye da 30 suka nutse bayan wani kwale-kwale ɗauke da mutane ya kife a kogin Dundaye a ƙaramar hukumar Wamakko da ke jihar Sokoto.

Lamarin ya faru ne ranar Lahadi da safe, lokacin da mutanen suka shiga kwale-kwalen domin zuwa gonakinsu.

Shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa ta NEMA mai lura da jahohin Sokoto da Kebbi da Zamfara, Aliyu Shehu-Kafindangiya, ya tabbatar wa da BBC aukuwar lamarin, inda ya ce, jami’an hukumar da gwanayen ninƙaya a ruwa na ƙoƙarin ceto sauran fasinjojin da ba a gani ba.

”Lamarin ya faru da misalin ƙarfe 10:00 na safe, kuma mun zo da jami’anmu da kuma gwanayen nutso a ruwa domin a san yadda za a ceto waɗannan mutanen da ke cikin ruwa, yanzu dai an fiddo gawa guda kuma an wuce da shi gida domin a yi masa sutura kamar yadda addini ya tanada”, in ji jami’in hukumar NEMA, Aliyu Shehu-Kafindangi.

Matuƙin kwale-kwale wanda shi kaɗai ne da ya tsira, ya shaida wa BBC cewa suna kan hanyarsu ne daga garin na Dundaye zuwa fadama domin aikin shinkafa lokacin da lamarin ya faru.

Wannan na zuwa ne ‘yan kwanaki bayan wani kwale-kwale ɗauke da fasinjoji aƙalla 20 ya kife a jihar Jigawa, lamarin da ya janyo mutuwar aƙalla mutum 15.

Hatsarin kwale-kwale a Najeriya, wani abu ne da ke neman zama babban bala’i, wanda masana ke dangantawa da rashin ingancin jiragen da kuma ƙazamin lodi da ake yi wa kwale-kwalen.

newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...
X whatsapp