Kafafen yada labarai a Japan sun ruwaito cewa, za a yi wa mutumin da ake zargin ya harbe tsohon firaministan kasar Shinzo Abe, gwajin kwakwalwa.
Gwajin kwakwalwar da za a yi masa, shi zai tabbatar da cewa, ko zai iya fuskantar shari’a kan laifin kisa.
Ana hasashen cewa mutumin dan shekara 41, ya kai hari ga Mista Abe ne saboda firaministan ya jajanta wa cocin Unification kan abin da ya faru da su, wanda kuma ake kiran mabiyansa da Moonies.
Wanda ake zargin ya fada wa masu bincike cewa taimakon kudi da mahaifiyarsa ta bai wa cocin, ya jefa su iyalan cikin matsin kudi. In ji BBC.