fidelitybank

Mutumin da ya doke Dangote a kudin Afrika

Date:

Attajirin nan ɗan ƙasar Afirka ta Kudu, Johann Rupert ya zarce attajirin nan ɗan Najeriya, Aliko Ɗangote a matsayin wanda ya fi kowa arziƙi a nahiyar Afirka, kamar yadda mujallar Bloomberg Billionaires Index.

Mista Rupert shi ne mai kamfanin Richemont wanda ɗaya ne daga cikin manyan kamfanonin da ke samar da kayan alatu da suka haɗa da shagunan Cartier and Montblack da ke sayar da turaren da agoguna da sauransu.

Yawan kuɗin attajirin sun ƙaru zuwa dala biliyan 14.3 daga dala biliyan 1.9, abin ya sa ya zama mai kuɗin duniya na 147 inda ya bai wa Ɗangote na Najeriya tazarar mutum 12.

Arziƙin Ɗangote dai ya ragu ne da dala biliyan ɗaya da miliyan ɗari bakwai ($1.7bn) a shekarar nan ta 2024, abin da ya mayar da yawan dukiyarsa zuwa dala biliyan 13.4, in ji mujallar Bloomberg.

A yanzu haka shi wannan attajirin ɗan Afirka ta Kudu na zaune ne a birnin Cape Town a wani gidan ƙasaita sannan yana da wasu ƙarin gidajen a biranen Geneva da London.

Nicky Oppenheimer, wanda shi ma ɗan Afirka ta Kudun ne shi ne mutum na uku da ke biyewa Ɗangote a masu kuɗin nahiyar Afirka, inda aka ƙimanta yawan dukiyarsa a kan dala biliyan 11.3.

Sai kuma Nassef Sawiris ɗan ƙasar Masar ne ke biye masa da arziƙi mai yawan dala biliyan 9.48. Sai kuma Natie Kirsh shi ma ɗan Afirka ta Kudu da ya zama na biyar a masu kuɗin Afirka inda yake da arziki mai yawan dalar Amurka biliyan 9.22.

Kamar dai mujallar Forbe, ita ma Bloomberg tana amfani da sauye-sauyen da ake samu a hawa da saukar dukiyar attajirai lokaci zuwa lokaci.

Kambun mutumin da ya fi kowa arziƙi na Afirka ka iya ci gaba da sauyawa a tsakanin attajiran bisa la’akari da yadda kasuwa ke jujjuyawa.

taraba state today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp