fidelitybank

Mutumin da ake zargi da kashe Matar kaninsa ya shiga hannu a jihar Jigawa

Date:

Rundunar ƴansanda a jihar Jigawa sun ce, sun kama wani mutum bisa zargin kashe matar ƙaninsa a ƙauyen Gunka da ke karamar hukumar Jahun a jihar.

Wata sanarwa da kakakin ƴansandan jihar SP Lawan Shiisu Adam ya fitar ranar Alhamis, ya ce ana zargin mutumin mai suna Buhari Sule mai shekara 25 da far wa matar ƙanin nasa – inda ya lakaɗa mata shegen duka har ta kai ga mutuwarta.

Sai dai ya ce ana tunanin cewa ba shi da lafiyar kwakwalwa, saboda baya ga kashe matar, ya kuma raunata ɗiyar makwabciyarsa ta hanyar yi mata duka da taɓarya.

Sanarwar ƴansandan ta ce lamarin ya faru ne ne ranar Laraba, 23 ga watan Afrilu da misalin karfe 5:30 na yamma a ƙauyen na Gunka.

“Bayan da muka je wurin da lamarin ya faru ne muka garzaya da waɗanda lamarin ya rutsa da su zuwa babban asibitin Jahun domin yi musu magani. Sai dai ɗaya daga cikinsu ta mutu a asibitin yayin da ɗayar kuma ke samun kulawa,” in ji Shiisu Adam.

Ya ce wanda ake zargin yana hannunsu a yanzu kuma suna ci gaba da bincike.

daily 
post news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp