fidelitybank

Mutumin da ake zargi da cinnawa ƴaƴan matarsa wuta ya shiga hannu

Date:

Rundunar ‘yan sanda a jihar Ondo, ta kama wani mutum bisa zargin kunnawa ‘ya’yan matarsa wuta.

Jami’in hulda da jama’a a rundunar ‘yan sandan jihar SP Funmilayo Odunlami ya tabbatar wa da kamfanin dillancin labaran kasar faruwar lamarin a Akure babban birnin jihar.

Ya ce lamarin ya faru ne ranar Asabar, inda ya ce jami’an ‘yan sanda suna gudanar da bincike, yayin da yaran ke samun kulawar likitoci a babban asibitin Owo.

Ya kara da cewa an mayar da batun zuwa ga sashen binciken manyan laifuka na rundunar ‘yan sandan jihar, domin gudanar da bincike yadda ya kamata.

Wani shaida ya fada wa kamfanin dillacin labaran kasar NAN cewa, mutumin ya kunna wuta a dakin da yaran ke kwance ne sakamakon samun ‘yar rashin jituwa da matar tasa.

Majiyar ta kara da cewa daya daga cikin yaran ya rasa ransa, sakamakon wutar.

nasarawa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...
X whatsapp