fidelitybank

Mutum uku sun rasu a hanyar Bauchi zuwa Kano

Date:

Da sanyin safiyar ranar Litinin ne wasu maza biyu da yarinya mace daya suka rasa rayukansu a wani hatsarin mota daya tilo da ya afku a kauyen Gada Data dake kan hanyar Bauchi zuwa Kano a karamar hukumar Ganjuwa a jihar Bauchi.

Wasu fasinjoji tara na wata motar bas ta Hummer dauke da fasinjoji 22 sun samu raunuka daban-daban a hadarin, wanda aka ce ya faru ne da misalin karfe 12:13 na safe.

Rahoton da hukumar kiyaye haddura ta kasa (FRSC) reshen jihar Bauchi ta fitar ta bayyana cewa, motar bus din kasuwanci na dauke da lamba: GKA519 XA.

Karanta Wannan: Mutane 15 sun mutu a hanyar Kogi – FRSC

Rahoton ya nuna cewa an kai rahoton afkuwar hatsarin ga jami’an hukumar bayan mintuna 10 da faruwar lamarin, inda nan take aka tura jami’an kiyaye haddura zuwa wurin domin gudanar da aikin ceto.

Ya kara da cewa jami’an sun garzaya da wadanda lamarin ya rutsa da su: manya maza biyar, manya mata uku, yara maza biyu da yara mata zuwa asibitin koyarwa na jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBUTH) da ke Bauchi, inda likita ya tabbatar da rasuwar marigayin.

Wadanda suka jikkata a cewar rahoton sun hada da manya maza uku, manyan mata uku, yara maza biyu da mace daya.

Daga nan ya bayyana cewa an ajiye gawarwakin wadanda suka mutu a dakin ajiye gawa na ATBUTH, inda kuma za a mika su ga ‘yan uwansu domin yi musu jana’iza.

naija hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi É—an shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin Æ´an Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taÉ“a barin Iran ta Æ™era makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaÆ™i – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama É—an kasar China da zargin kai wa Æ´an Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp