Mutane hudu ‘yan gida guda ne suka nutse a hatsarin kwale-kwale a jihar Kebbi.
Hukumomi da mazauna yankin sun ce waɗanda hatsarin ya rutsa da su suna hanyarsu ta zuwa gona tsallaken rafi a lokacin da kwale-kwalen da suke ciki ya kife a ranar Laraba a yankin Yauri sakamakon iska mai ƙarfin gaske.
Mutum shida ne ke cikin kwale-kwalen, wani uba Musa Labaran da ƴaƴansa.
Ya shaida wa BBC cewa, an samu gawar ƴaƴansa hudu yayin da ake ci gaba da neman gawar mutum na biyar da ba a gani ba.
An sha samun hatsarin kwale-kwale a Najeriya
A watan Mayun shekarar da ta gabata, sama da mutum 100 ne suka nutse a ruwa lokacin da kwale-kwalen da suke ciki ya kife a jihar Kebbi yayin da a cikin watan Disamba kimanin mutum 30 suka mutu a wani hatsari makamancin haka a jihar Kano.
Ana danganta irin wannan al’amari ne da yadda ake loda wa kwale-kwale kaya da mutane da suka wuce ƙima da rashin kula da jiragen na ruwa da kuma rashin kyawun yanayi.