Mutum huɗu sun mutu sakamakon rikici game da wani fili tsakanin garuruwa biyu na jihar Ebonyi da ke kudu maso gabashin Najeriya.
Kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN ya ruwaito cewa rikicin ya ɓarke ne tsakanin mazauna ƙauyukan Ogwor da Umuobor saboda wani yanki da ake kira Elueke.
Rahoton ya ce gwamnatin jihar ta ayyana yankin a matsayin “ba na kowa ba” a farkon watan Janairu, kuma ta umarci duka ƙauyukan su ƙaurace wa yankin.
“Daga cikin mutum huɗu da aka kashe, an ce uku sun je nome doya ne a yankin ranar Laraba, kafin a kashe wata mace a ranar Litinin,” a cewar Chinasa Okorie, shugaban cibiyar Akaeze Development.
Sai dai kakakin rundunar ‘yansanda a jihar, Joshua Ukandu, ya ce kisan wata mace kawai suka sani a ranar Litinin da ta gabata, amma ya ce suna ci gaba da bincika lamarin.