Rikicin da ya sake barkewa tsakanin wasu kungiyoyin asiri biyu ya yi sanadin mutuwar mutane hudu, yayin da aka kone gidaje kusan biyar a yankin Kabawa da ke karamar hukumar Lokoja, babban birnin jihar Kogi.
Jaridar THISDAY ta samu tabbataccen cewa, rikicin ya samo asali ne a daren ranar Litinin din da ta gabata a lokacin da kungiyoyin biyu masu gaba da juna da mambobi ‘yan kasa da shekaru 13,14, da kuma shekaru 15 suka tsunduma kansu cikin neman ‘yanci, wanda ya yi sanadin kashe-kashe da kona gidaje a Kabawa, wani yanki na asali.
Rikicin da ya ki ci ya ki cinyewa ya sa mazauna yankin sun kwashe iyalansu daga yankin zuwa wani wuri, domin yin hijirar dole, saboda gujewa fadawa cikin rikicin.
Majiyoyin cikin gida sun yi nuni da cewa, rikicin ya samo asali ne sakamakon ramuwar gayya da wata kungiya ta yi bayan kashe daya daga cikin mambobinsu.
Majiyar ta kara da cewa ‘yan ta’addan wadanda ke dauke da bindigu da wasu muggan makamai sun mamaye wasu gidaje, inda suka far wa mutane tare da kona gidajen da suke kyautata zaton ‘yan kungiyar ne.
Sai dai yayin da ‘yan sanda suka mamaye yankin a jiya, domin kwantar da hankulan, wasu daga cikin ‘yan kungiyar asiri sun yi ta artabu da jami’an tsaro, wanda ya dauki tsawon sa’o’i da dama kafin daga bisani a samu nasara. An tattaro cewa wasu daga cikin ‘yan kungiyar asiri sun tsallake rijiya da baya a cikin kogin Nijar, domin gudun kada ‘yan sanda su kama su, suka tsallaka zuwa wancan gefen kogin.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Kogi, SP William Aya, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce, rundunar ta kama mutane 15 da ake zargi.
Aya ya bayyana cewa, rundunar ta tabbatar da cew, an kashe mutum daya ne kawai
ana ci gaba da binciken abin da ya kai ga faruwar lamarin.